05/11/2022
Idan baku san waye Annabinmu ba, bari mu gaya muku SHI ﷺ.
- Shi 'Dan Adam ne amma yafi Adam daraja. Kuma da za'a dunkule dukkan halittu awaje guda, shi kadai ya fisu ya zarcesu. Domin kuwa Adamu (alaihis salam) da dukkan zuriyarsa suna karkashin tutar Annabinmu aranar Alkiyamah.
- Duk da cewa ba ya zanen rubutu ko karanta karatu to amma yafi dukkan masu ilimi sanin ilimi domin shine Malamin dukkan malamai.
- Wajen kyawun halaye da dabi'u kuwa, wallahi duniya bata ta'ba ganin tamkarsa ba, awajen gaskiya da rikon amana da juriya.
Wajen Hakuri kuwa, ya jure wahalar da ta zarce abinda sauran Annabawa s**a riska. Ga afuwa ga saurin yafewa, ga baiwa ga karamci da alfarma.
- Wajen Tawadhu'u kuwa, duk da cewa yafi kowa daraja amma bai taba yin girman kai ba, b***e yace maka yafi wane.
-Yana zama da talakawa da miskinai, yana zuwa gaisar da marassa lafiya, yana cin abinci tare da bayi da miskinai. kuma yana sanya duk irin tufafin da ya samu gareshi.
- Bai taba raina wani mutum ba, bai taba kushe abinci ba, kuma bai taba yin rowa ba.
Wajen karamci da mutunci kuwa, ba zaka taba ganin tamkarsa ba.
Wajen tsaftar jiki da tsaftar halaye da dabi'u, dukkan masu tsafta dashi suke yin koyi.
Wallahi harshen masu yabo ya gaza wajen tantance matsayinsa. Kamar yadda alkaluman masu rubutu sun kasa kaiwa mutuqa wajen bayann kaifiyyarsa ﷺ.
Qurewar kalmar da zaka fa'da akansa ita ce kace masa CIKAKKEN BAWAN ALLAH, kuma HUJJAR ALLAH AKAN DUKKAN HALITTUNSA ﷺ.
Ya Allah yi cikakkun salatai da tasleemai marassa yankewa bisa Shugabanmu Annabinmu Muhammadu tare da iyalan gidansa tsarkaka da Sahabbansa amintattu da dukkan Salihan bayinka har zuwa ranar sakamako.
DAGA ZAUREN FIQHU 07064213990(17/10/1443 18/05/2022)